Najeriya za ta dauko Bature kocin Eagles
Shugaban hukumar kwallon kafa a Najeriya Amaju Pinnick ya dage kan lalle sai bature zai dauko domin horar da ’yan wasan Super Eagles, wannan na zuwa ne bayan haramtawa kasar shiga gasar cin kofin nahiyar Afrika a badi.
Wallafawa ranar:
Pinnick yace ba zai yi wasa da gasar cin kofin duniya ba da za a yi a Rasha a 2018, don haka ya zama wajibi a dauko kwararre daga waje.
Ya kare matakinsa, yana mai cewa sun gwada na gida amma ba wata riba.
An ba Sunday Oliseh dama, sannan aka dawo da Siasia wanda ya gaza doke Masar da ta haramtawa Najeriya zuwa Afcon.
Rahotanni dai na cewa tuni hukumar kwallon kafar ta Najeriya da dauki baturen Faransa da ba a bayyana sunansa ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu