CHAN 2016: An fitar da Najeriya da Nijar a Rwanda
An yi waje da Najeriya da Nijar a gasar cin kofin Afrika ta matasa da ake gudanarwa a Rwanda bayan sun sha kashi a wasan karshe da aka fafata a rukuninsu na C.
Wallafawa ranar:
Najeriya ta sha kashi ne hannun Guinea ci 1 da 0 wanda ya ba Guinea nasarar kai wa zagaye na gaba. Ibrahim Sankhon ne ya jefa Guinea kwallo a ragar Najeriya.
Tunisia kuma ta casa Nijar ne 5 da 0 wanda ya ba kasar nasara kai wa zagaye Kwata Fainal.
Tuni dai Kamaru ta tsallake zuwa zagayen kwata fainal a gasar bayan ta doke Jamhueriyyar Congo ci 3 da 1 a rukuninsu na B.
Yanzu kuma Kamaru za ta hadu ne da Cote d’Ivoire a kwata fainal.
Jamhuriyyar Congo kuma da ke bi mata a saman teburin rukuninsu zata kara ne da Rwanda mai masaukin baki
A ranar Asabar ne za a yi fafatawar a filin wasa na Amahoro a Kigali.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu