Kwallon Kwando
Najeriya ta lashe gasar kwallon Kwando a Afrika
‘Yan wasan kwallon kwando D Tigers na Najeriya sun lashe gasar Afrika da aka gudanar a Tunisia bayan sun doke Angola a wasan karshe ci 74 da 65.
Wallafawa ranar:
Talla
Wannan ya ba ‘Yan wasan na Najeriya nasarar wakiltar Afrika a wasannin Olympic da za a gudanar a Brazil a badi.
Wannan ne karon farko da Najeriya ta lashe kofin gasar na kwallon Kwando a Afrika.
Tunisia ce ta zo a matsayi na uku bayan ta doke Senegal a ranar Assabar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu