CAF
Morocco ta shigar da kara
Hukumar kwallon Morocco ta shigar da kara a kotun sauraren koken wasanni domin kalubalantar CAF kan dakatar da kasar daga shiga gasar cin kofin Afrika guda biyu bayan ta ki karbar bakuncin gasar saboda tsoron Ebola.
Wallafawa ranar:
Talla
Baya ga haramcin kuma CAF ta ci Morocco tarar kudi dala Milayan guda.
Kakakin hukumar kwallon Morocco Mohammed Makrouf ya ce sun kai kokensu a kotun wasanni, domin a cewarsa suna da damar kalubalantar hukuncin.
Tuni dai Morocco ta yi watsi da hukuncin na CAF saboda matakin zai gurgunta harakokinta na kwallon kafa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu