Isa ga babban shafi
CAF

CAF ta dakatar da Morocco daga shiga gasar cin kofin Afrika

Hukumar CAF da ke kula da kwallon Kafa a Afrika ta dakatar da kasar Morocco daga shiga gasar cin kofin Afrika da za a gudanar a 2017 da 2019 bayan kasar ta ki karbar bakuncin gasar da ake gudanarwa a kasar Equatorial Guinea saboda tsoron cutar Ebola.

Shugaban kwallon Afrika Issa Hayatou.
Shugaban kwallon Afrika Issa Hayatou. AFP PHOTO/FADEL SENNA
Talla

CAF kuma ta ci tarar Morocco kudi dalar Amurka miliyan guda.

CAF ta dauki wannan matakin ne a kan Morocco bayan an kai zagayen karshe a gasar cin kofin Afrika da Equatorial Guinea ta karbi bakunci.

A ranar Lahadi kasar Cote’Ivoire za ta fafata da Ghana a wasan karshe.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.