Manchester United za ta fuskanci kalubalen da ba ta taba fuskanta ba – Rio Ferdinand
Dan wasan Manchester United Rio Ferdinand ya ce kungiyar za ta fuskanci kalubalen da ba ta taba fuskanta ba a tashin farko a Gasar Premier saboda wasannin guda biyar na farko da za su buga a sabuwar kakar wasa da za a shiga sun hada da karawa da kungiyoyin Chelsea, da Liverpool da kuma Manchester City.
Wallafawa ranar:
Man U. za ta fara karawa ne da Swansea City a ranar 17 ga watan Agusta inda za ta kai mata ziyara, wanda kuma Ferdinand din ya ce jan aiki ne.
Kungiyar ta Manchester kamar yadda rahotanni ke nunawa ta bayyana cewa kungiyoyin Chelsea da Manchester City sun kasance kungiyoyin da za su iya kawo musu cikas wajen ci gaba da mallake kofin gasar ta Premier.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu