Isa ga babban shafi

Kasashen yankin Caribbean sun kira taron gaggawa kan rikicin Haiti

Shugabannin kasashen yankin Caribbean sun yi kira da a gudanar da wani taron gaggawa a Jamaica tare da kasashen Amurka, Kanada da Faransa a gobe Litinin don neman hanyar fita daga tarzomar 'yan tawayen Haiti.

Mambobin kungiyar sun kwashe watanni suna kokarin ganin 'yan siyasa a Haiti sun amince da kafa gwamnatin hadin kan kasa ta rikon kwarya.
Mambobin kungiyar sun kwashe watanni suna kokarin ganin 'yan siyasa a Haiti sun amince da kafa gwamnatin hadin kan kasa ta rikon kwarya. REUTERS - RALPH TEDY EROL
Talla

Mambobin kungiyar sun kwashe watanni suna kokarin ganin 'yan siyasa a Haiti sun amince da kafa gwamnatin hadin kan kasa ta rikon kwarya.

Duk da cewa kungiyar ta kasashe 15 ba ta yi nasara ba izuwa yanzu, cikin wata sanarwa da ta fitar a yammacin Juma'a da ta gabata, ta ce har yanzu ta na kan bakanta na neman cimma wannan manufa.

Ko a ranar Jumma'a da ta gabata sai da gungun tsagerun 'yan Haiti masu adawa da gwamnati suka yi fito-na-fito da 'yan sandan kasar, rikicin da ya tilasta kungiyar kasashen na Caribbean kiran taron gaggawa domin kawo karshen wannan fita da ke neman daidaita kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.