Isa ga babban shafi

Faransa ta cafke wasu mutane 5 da take zargi da kitsa ta'addanci a kasar.

Mutane 5 ne aka kama a ranar juma’ar da ta gabata a yankin gabashin kasar Faransa,  inda ake ci gaba da tsaresu a karkashin rundunar ma’aikatar leken asiri, a wani binciken ayukan ta’addanci da ta ke tuhumarsu da aikatawa, kamar yadda mai shigar da karar ayukan ta’addanci ya sanar.

ministan cikin gidan Faransa Gerald Darmanin, na tattaunawa da wasu yan sanda lokacin da ya kai  ziyara a cibiyar yan sanda dake Les Mureaux,dake wajen birnin paris, laraba 7 Yuli 2020.
ministan cikin gidan Faransa Gerald Darmanin, na tattaunawa da wasu yan sanda lokacin da ya kai ziyara a cibiyar yan sanda dake Les Mureaux,dake wajen birnin paris, laraba 7 Yuli 2020. AP - Thomas Samson
Talla

Wata majiyar ta kusa da kundin,  ta sanar da AFP cewa, an kanga wa mutanen 5 kyaure ne, ba tare da yin wani karin haske kan irin zargin da ake yi masu ba.

A cewar majiyar, an yi kamun ne a safiyar ranar juma’ar da ta gabata a cikin gundumomin Meurthe-da-Moselle, dake cikin jihar Nancy, da kuma garuruwan dake kusa da juna,  Vandœuvre-lès-Nancy da  Toul. 

Shi dai wannan samame ya zo ne a dai dai lokacin da ministan cikin gida Gérald Darmanin,   a ranar juma’a ya yi kiran kantomomi, da su maida hankali sosai kan lamarin tsaro,  albarkacin shagulgulan Christmas da sauran shagulgulan addinin da ake gudanarwa, sakamakon karuwar barazanar ayukan ta’addanci da ake ci gaba da  fuskanta a kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.