Isa ga babban shafi

Gobarar daji: Kimanin mutane dubu 30 ne aka umurta su bar yammacin Canada

Gobarar daajin da ta  addabi yamacin Canada ta ta’azzara a jiya Lahadi, a yayin da aka yi ta kwashe mazauna yankunan da abin ya shafa daga gidajensu zuwa tudun mun-tsira.

Yankin British Colombia kena na Canada, inda gobarar daji ta yi tilasta wa mutane barin gidajensu.
Yankin British Colombia kena na Canada, inda gobarar daji ta yi tilasta wa mutane barin gidajensu. © AP - DARRYL D
Talla

Wutan da ke ci gaba da ci ba kakkautawa, tana barazana ga dimbim yankuna a kwarin Okanagan, ciki har da birnin  Kelowna, a yankin British Columbia.

Mahukuntan yankin sun bayyana lamarin a matsayin mai tayar da hankali, inda aka jiyo ministar kula da agajin gaggawa Bowinn Ma tana shawartar  masu yawon bude ido da su guji zuwa inda gobarar ta shafa.

Kimanin mutane dubu 30 ne ake kwashewa zuwa tudun mun-tsira, a yayin da  wasu karin dubu 36  ke cikin jiran umurnin arcewa.

dubban mutanen dake kewayen yankin, da kuma wasu a yammacin garin Kelowna sun baar gidajensu tuni, kuma suna zama a sansanoni da otel-otel ko kuma da ‘yan uwa da abokai, a yayin da a sauran biranen  ake jira  ko za a ji umurnin cewa kowa ya bar inda yake.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.