Turai za su kare yarjejeniyar Iran daga lalacewa
Shugabannin kasashen Turai sun amince da daukar matakin bai daya domin kare yarjejeniyar nukiliyar Iran bayan ficewar kasar Amurka.
Wallafawa ranar:
Shugabannin sun sha alwashin bai wa Iran duk taimakon da take bukata muddin ta ci gaba da mutunta yarjejeniyar da ta kulla a shekarar 2015. Shugabannin na kasashen Turai 28 sun bayyana cewar za su ci gaba da kare kasar Iran daga duk wata barazana muddin ita kuma ta ci gaba da mutunta yarjejeniyar da ta kulla.
Shugabannin sun amince da shirin kare kamfanonin kasashen Turai da tuni suka samu kwangiloli a Iran domin kaucewa takunkumin da Amurka ta sanyawa kasar.
Taron ya kuma amince kan yadda zai magance matsalar cewar Iran na fadada ikon ta a gabas ta tsakiya da gina makamai masu linzami da kuma abinda zai biyo baya lokacin da yarjejeniyar nukiliyar za ta daina aiki a shekarar 2025.
A karshe shugabannin sun amince su mayar da martini kan harajin da Trump ya sanya musu wajen cinikin karafa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu