Isa ga babban shafi
Amurka

An wanke Trump daga zargin alaka da jami'an Rasha

Kwamitin majalisar wakilan kasar Amurka, da aka dorawa alhakin bincika zargin hadin bakin jami’an Rasha da kwamitin yakin neman zaben shugaba Trump a 2016, ya ce babu wata shaida da ke nuna zargin da ake yi ya tabbata.

Shugaban Amurka Donald Trump.
Shugaban Amurka Donald Trump. REUTERS/Yuri Gripas
Talla

Kwamitin, wanda ya bayyana rahoton nasa a jiya Juma’a, ya ce babu shaidar da ke nuna cewa yarjeniyoyin kasuwanci da Donald Trump ya kulla da wasu kamfanonin Rasha, sun zama tsani ga samar da hadin baki tsakanin yakin neman zabensa da jami’an kasar ta Rasha.

Sai dai rahoton kwamitin ya nuna cewa akwai makusantan Trump da suke da alaka da wasu jami’ai a kasar ta Rasha masu dauke da alamar tambaya.

Shugaban Amurka Donald Trump ya dade yana musanta zargin da ake na hadin baki tsakanin kwamitin yakin neman zabensa da wasu jami’an Rasha a shekarar 2016, wajen kayar da abokiyar hamayyarsa Hillary Clinton a zaben shugabancin kasar.

Cikin sakon da ya wallafa a shafinsa na twitter bayan da kwamitin ya fitar da rahoton, Trump ya bayyana cewa hakan ya kawo karshen bita da kullin da ake dade ana yi masa.

Sai dai ‘yan majalisar wakilan Amurkan daga jam’iyyar Democrats guda 9 da ke cikin kwamitin mai manbobi 22, sun yi watsi da sakamakon rahoton da aka wallafa.

‘Yan majalisar na jam’iyyar Democrats sun zargi takwarorinsu na Repulican da kaucewa bin hanyoyin da suka dace wajen gudanar da bincike akan zargin hadin bakin, tsakanin Trump da jami’an Rasha.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.