Trump ya fara sharar fagen sake neman shugabanci
Shugaban Amurka Donald Trump ya nada Brad Parscale a matsayin Manajan yakin neman zaben sa wa’adi na biyu da za’ayi a shekarar 2020.
Wallafawa ranar:
Ofishin yakin neman zaben Trump, ya ce Parscale mai shekaru 42, zai mayar da hankali wajen shirya matakan da za’a bi wajen gudanar da yakin neman sake zaben shugaban da kuma fatan samun nasara.
Yayin da yake amsa tambayoyi a gaban zauren majalisar Amurka, Parscale, wanda ya taba zama daya daga cikin jami’an yakin neman zaben Trump a shekarar 2016, ya musanta cewa an samu hadin baki tsakaninsu da wakilan kasar Rasha, domin tasiri a zaben da ya gudana.
Wannan mataki dai na zuwa ne kasa da shekara guda da rabi da Trump ya yi, da fara shugabancin Amurka.
Amurkawa da dama basu yi mamakin bayyana aniyar shugaban nasu na neman a sake zabensa ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu