Zan so na amsa tambayoyi daga masu bincike-Trump
Shugaban Amurka Donald Trump ya ce a shirye yake ya amsa tambayoyi daga Robert Mueller, mai bincike na musamman kan katsalandar din ƙasar Rasha cikin zaben Amurka na shekarar 2016.
Wallafawa ranar:
Lokacin da ya zanta da manema labaru a fadar White House, Trump ya ce zai rantse sannan ya amsa tambayoyin da za a yi masa.
Shugaban na Amurka ya tabbatar da cewa lauyoyinsa na tattaunawa da Mueller kan yiwuwar haɗin baki tsakanin Trump da Rasha wajen yin katsalandan cikin sakamakon zaɓen, da kuma zargin da ake yi masa na kokarin yin zagon-ƙasa ga binciken.
Ya ce zai tattauna da masu binciken da zarar lauyoyinsa suka ba shi izini yin hakan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu