Isa ga babban shafi
EU

Kungiyar EU ta fara taro kan gaggauta tattaunawar ficewar Birtaniya

Yau Alhamis shugabannin kungiyar kasashen Turai 28 ke gudanar da taro a Brussels, inda zasu duba yadda tattauna ke gudana tsakanin wakilan kungiyar da na gwamnatin Birtaniya mai kokarin ficewa daga cikin ta.

Ministan lura da tattaunawar ficewar Birtaniya daga kungiyar tarayyar turai, David Davis, da kuma Michel Barnier, shugaban kwamitin sasantawa ko mai shiga tsakani na tattaunawa tsakanin EU da Birtaniya a birnin Bruxelles ranar 25 Satumba 2017.
Ministan lura da tattaunawar ficewar Birtaniya daga kungiyar tarayyar turai, David Davis, da kuma Michel Barnier, shugaban kwamitin sasantawa ko mai shiga tsakani na tattaunawa tsakanin EU da Birtaniya a birnin Bruxelles ranar 25 Satumba 2017. REUTERS/Francois Lenoir
Talla

Ana kuma sa taron ya amince da shirin bada kudade domin dakile yadda baki ke kwarara zuwa Turai, musamman daga nahiyar Afrika.

Kungiyar kasashen Turai tace ya zuwa yanzu babu wani ci gaba da aka samu a tattaunawar rabuwa tsakaninta da Birtaniya duk da cewa an kwashe watanni 5 ana yi.

Shugaban kungiyar Donald Tusk wanda ya bayyana shakku dangane da cimma wata yarjejeniya a taron na yau, yace har yanzu Birtaniya ta gaza wajen gabatar da kwararan bukatun ta.

Tusk yace cikin kudirorin da har ya zuwa yanzu ba’a cimma matsaya akan su hada da makomar Yan kasashen Turai dake zama a Birtaniya da batutuwan da suka shafi Ireland ta Arewa, sai kuma kudaden rabuawa da kungiyar ke bukatar Birtaniya ta biya.

A wani cigaban kungiyar tayi alkawarin samar da kudade domin gudanar da wasu ayyuka a wasu kasashen Afirka cikinsu harda Nijar domin hana baki tsallakawa Turai da kuma samar da ci gaba a Yankin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.