Taron samar da hanyoyin magance matsallar yan cin rani a Turai
A gobe lahdi ministocin cikin gida na kasashen Faransa,Italia, da Jamus za su gudanar da wani taro a Paris domin duba wasu daga cikin matsallolin dake hana ruwa gudu dangane da batun bakin haure.
Wallafawa ranar:
Taron dake zuwa bayan da rahotanni daga Hukumar Kula da harakokin bakin haure ke cewa an fidda tsamanin samun wasu mutane 60 bakin haure da kwale-kwaeln da suke ciki ya nutse bayan sun bar gaban tekun Libya.
Wani wanda ya tsallake rijiya da baya daga cikin kwale-kwalen ya bayyana cewa akwai mutane tsakanin 140 zuwa 160 da suka hada da mata a lokacin da kwale-kwalen ya fara tangal-tangal zai nutse.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu