Isa ga babban shafi
Britaniya- Poland

Fira Ministan Britaniya ya yi gargadi a guji nuna kyamar baki

Fira Ministan kasar Britaniya David Cameron ya gargadi mutan kasar da su guji nuna duk wata kyamar baki bayan da aka yi zaben raba-gardama dake nuna an fi kaunar ficewa daga cikin kungiyar Tarayyar Turai.

Fira Ministan Britaniya  David Cameron tare da matar sa  Samantha a lokacin da zasu tafi jefa kuriar raba gardama ranar 23 Yuni 2016.
Fira Ministan Britaniya David Cameron tare da matar sa Samantha a lokacin da zasu tafi jefa kuriar raba gardama ranar 23 Yuni 2016. REUTERS/Stefan Wermuth
Talla

Fira Minista David Cameron wanda yake Magana da manema labarai ta bakin kakakin sa , ya ce Gwamnatin Britaniya ba zata amince da muzgunawa baki ba, da wasu ‘yan son iyawa suka fara nunawa.

A dan tsakanin nan ne  Ofishin jakadancin Poland a Landan ya bayyana damuwa saboda wasu kalamai da takala da ake yi wa al'ummar Poland mazauna Landan.

Acewar Ofishin Jakadancin Poland a Landan wasu har aike masu da wasiku suke yi ana zolayansu wai su koma 'kasar EU ba kasar Britania ba'.

Magajin garin birnin Landan Sadiq Khan tuni dai ya sanar da jami'an tsaro domin ganin sun sa ido kada wasu su janyo tarzoma a kasar.

Jami'an tsaro a Landan sun bayyana cewa suna nazarin irin wasiku da wasu suka rubuta inda suke nuna kyamar baki bayan zaben raba gardama da aka gudanar makon jiya.
Shi kansa Ministan kudi na Britania George Osborne ya ja kunnen masu nuna kyamar baki inda yake cewa Britaniya ba'a san ta da nuna kyama ba.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.