Isa ga babban shafi
TANZANIA

Ana zargin wasu mutane biyar da kashe matukin jirgin Britaniya a Tanzania

Shugaban kasar Tanzania John Magufuli ne ya bayar da umarnin kama wasu yan kasar biyar bisa laifin kakkabo helikoptar dan kasar Britaniyan a yayin da yake kokarin hana su cire hauren giwaye da aka kashe a gidan namun dajin Maswa dake arewacin kasar

Tarin hauren giwa
Tarin hauren giwa REUTERS/Tiksa Negeri
Talla

Matukin jirgin helikoptar mai suna Roger Gower yana da shekaru 37 kuma ya gamu da ajalinsa ne a yayin da yake kokarin hana wadanan mutanen masu fataucin hauren giwa da suka kewaye wasu gawarwakin giwaye a wani yankin gidan ajiye namun daji mai suna Maswa a arewacin kasar daga cire hauren giwayen.

Gower dai ya dadde yana aikin kare namun daji a Tanzania inda yake adawa da fataucin hauren giwa a wani mataki na ganin ba’a karas da wannan rukunin na dabbobi daga doron kasa ba.

Shugaba Magufuli ya bayyana al’amarin a matsayin abin takaici inda ya kuma sha alwashin hukunta duk wani wanda aka samu da hannu a kisan Mr Roger Gower, kwararru dai na ci gaba da gargadin kaucewa gushewar Giwaye daga doron kasa.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.