Isa ga babban shafi
Turai

Maharin Brussels ya taba aiki a Majalisar Turai

Wani Bincike a Turai ya nuna cewar daya daga cikin mutanen da suka kai harin bam a Brussels wanda ya hallaka mutane 32 ya taba aiki a Majalisar kungiyar kasashen Turai.

Najim Laachraoui daya daga cikin wadanda ake zargi sun kai hari a Brussels
Najim Laachraoui daya daga cikin wadanda ake zargi sun kai hari a Brussels ©AFP/
Talla

Mai magana da yawun Mjalaisar, Jaume Duch Guillot, ya ce Maharin mai shekaru 25, ya yi aiki a matsayin mai shara a 2009 a karkashin wani kamfanin da aka bai wa kwangilar tsabtace Majalisar.

Sai dai ba a bayyana sunan shi ba, amma wata majiya kusa da masu bincike tace sunan maharin Najim Laachraoui.

Kakakin ya ce a lokacin da ya yi aiki babu wani tarihi akan shi na aikata laifi, amma ya tafi Syria a 2013.

Ana kuma zargin Najim Laachraoui yana da alaka da hare haren da aka kai a birnin Paris a watan Nuwamba inda aka kashe mutane 130.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.