Isa ga babban shafi
Belgium

An soke taron gangamin adawa da ta'addanci a Brussels

Hukumomin kasar Beligium sun bukaci al’ummar kasar da su kaurace wa halartar taron gangami da aka tsara gudanarwa a gobe lahadi domin yin tir da ayyukan ta’addanci.

taron gangamin nuna adawa da ayyukan ta'addanci a birnin Bruxelles ranar 23, 2016.
taron gangamin nuna adawa da ayyukan ta'addanci a birnin Bruxelles ranar 23, 2016. REUTERS/Christian Hartmann
Talla

Magajin garin birnin Brussels Yvan Mayeur, ya ce har yanzu akwai barzanar sake kai hare-hare a birnin, saboda haka bai kamata jama’a su halarci duk wani taro na gangami ba sai a cikin makonni masu zuwa.

Ministan cikin gidan kasar Jan Jambon ya goyi bayan wannan mataki da magajin garin Brussels ya dauka. Tuni dai wadanda suka shirya zanga-zangar suka amincewa da wannan mataki.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.