Isa ga babban shafi
Denmark

Denmark za ta takaita kwararar ‘Yan gudun hijira

Majalisar Denmark ta amince da sabbin dokokin rage kwararar baki ‘Yan gudun hijira da ‘yan ci rani, matakin da ya janyo suka ciki da wajen kasar.

Denmark da Sweden sun tsaurara matakan dakile kwararar 'yan gudun hijira
Denmark da Sweden sun tsaurara matakan dakile kwararar 'yan gudun hijira REUTERS/Pascal Rossignol
Talla

Sabbin dokokin ‘Yan Majalisa suka amince a yau Talata sun kunshi takaita ba bakin damar shigar da ‘yan uwansu bayan sun samu damar izinin zama a kasar.

Sannan za a kwace wasu kadarorinsu da suka mallaka a cikin kasar ta Denmark.

Matakin dai ya janyo suka a ciki da wajen kasar kan tsauraran matakan da Denmark ta dauka.

Gwamnatin kasar ta ce ya zama wajibi ta dauki matakin domin dakile kwararar baki yan gudun hijira.

Tuni dai Denmark da Sweden suka tsaurara matakai a kan iyakokinsu domin rage kwararar ‘yan gudun hijira mafi yawancinsu ‘yan kasashen Syria da Iraqi da Afghanistan da ke kauracewa yaki.

‘Yan rajin kare hakkin bil’adama dai sun yi kakkausar suka kan matakan da Denmark ke son dauka wanda suka ce ya sabawa dokin kasa da kasa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.