Isa ga babban shafi
Faransa

Faransa za ta fara ruguza runfunan ‘Yan ci-rani a Kurmin Calais

Hukumomin Faransa za su fara ruguza sansanin da ‘Yan ci rani suka kafa a yankin Calais da nufin tsallakawa zuwa Birtaniya, yayin da kasar za ta fara mayar da su cikin wani sansani da aka inganta don kare lafiyarsu da kuma samar da tsaro.

Dubban mutane ne ke rayuwa a sansanin Calais
Dubban mutane ne ke rayuwa a sansanin Calais REUTERS/Benoit Tessier
Talla

Gwamnatin kasar tace tana sa ran kwashe baki ‘Yan ci-ranin da ‘Yan gudun hijira tsakanin 500 zuwa 700 don mayar da su sabbin wuraren da ke da abubuwan more rayuwa da suka hada da wutar lantarki da na’urar dumama daki da kuma ta kula da jirirai.

Sai dai bakin na fargabar zuwa sansanin da aka samar saboda matakan tsaro musamman tantance masu shiga da fita.

Faransa da Birtaniya dai sun kashe makudan kudade domin inganta tsaro a kan iyakokinsu musamman yankin Calais inda dubban ‘Yan ci rani ke kokarin tsallakawa.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.