Kasashen Turai
Matsalar bakin haure ta ta’azzara a kasashen Turai
Wasu sabbin alkalumma da cibiyar kididdiga ta Tarayyar Turai ta fitar na tabbatar da cewa yawan masu bukatar mafaka ko kuma izinin shiga a matsayin ‘yan gudun hijira a Turai ya karu da kimanin 85 % a yankin daga bara zuwa bana.
Wallafawa ranar:
Talla
Rahoton ya ce kasar Jamus ce sahun gaba da masu bukatar irin wannan izini suka gabatar da bukatunsu, sai kasashen Hungry da Austria, yayin da Faransa ke a matsayin kasa ta uku.
Yanzu haka dai kasar Kuroshiya ta kange iyakarta da kasar Hungry inda dubban ‘yan gudun hijira ke kokarin tsallakawa zuwa cikin kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu