Isa ga babban shafi
Mexico

‘Yan ta’adda sun kashe ‘yan sanda 15 a Mexico

Hukumomin kasar Mexico sun ce wata kungiyar yan ta’adda ta kashe ‘Yan Sandan kasar 15 a wani kwantan baunar da suka yi musu a yammacin kasar

Omar Treviño Morales, capo del cartel Los Zetas, escoltado por militares durante una conferencia de prensa sobre su captura, el 4 de marzo de 2015.
Omar Treviño Morales, capo del cartel Los Zetas, escoltado por militares durante una conferencia de prensa sobre su captura, el 4 de marzo de 2015. REUTERS/Henry Romero
Talla

Kwamishinan tsaron Jihar Jalisco, Francisco Alejandro Solorio, ya ce an tare tawagar ‘yan Sandan ne akan hanyar su ta zuwa Guadalajara, inda nan take aka kashe 15 daga cikinsu, yayin da 5 kuma suka samu munanan raunuka.

Kasar Mexico na fama da kungiyoyin masu hada-hadar kwayoyi da kuma safarar su zuwa kasashen waje.

Matsalar safarar miyagun kwayoyi dai matsala ce da ta zame wa gwamnatocin kasa-da-kasa alakakai, inda suke ci gaba da daukar matakan kamewa da kuma gurfanar da wadanda ake samu da laifin.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.