An kona Ofishin Jam’iyya mai mulki a Mexico
Dubban matasa Dalibai masu zanga-zanga a kasar Mexico kan bacewar Dalibai 43, sun kona ofishin Jam’iyya mai mulkin kasar da ke a Jihar Guerrero, a ci gaba da fadadar tashin hankalin da ake samu a kasar
Wallafawa ranar:
‘Yan Sandan kwantar da tarzoma na kasar ta Mexico, sun yi arangama da masu-zanga zangar ne, lokacin da hayaki ya tirnike ginin jam’iyar Institutional Revolutionary Party a Jiahr Chilpancingo.
Masu zanga-zangar dai ne suka sakawa Ofishin Jam’iyyar Wuta, domin nuna rashin jin dadinsu da batan ‘yan Uwansu.
Cikin masu zanga zangar harda dalibai, kungiyar malamai, da kuma iyaye wadanda suka dinga jifan Yan Sanda.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu