Birtaniya
‘Yan sandan Birtaniya sun arangama da dalibai
‘Yan Sanda a Birtaniya sun yi arangama da dalibai masu zanga zanga a tsakiyar birnin London lokacin da suke zanga zangar adawa da Karin kudin makaranta da rage tallafin ilimi da gwamnati ke yi da kuma bashi. ‘Yan Sanda sun yi kokarin korar masu zanga zangar da suka nufi ofishin Jam’iyar Conservative suka kuma kutsa kai zuwa Majalisar kasa inda suke cewar suna bukatar gwamnati ta samar da ilimi kyauta.
Wallafawa ranar:
Talla
Rundunar ‘Yan Sanda tace ta kama 11 daga cikin daliban wadanda ake zargi da laifin kai hari kan jami’an tsaro.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu