Isa ga babban shafi
Faransa

Hollande zai sha kaye a zaben 2017-bincike

A wani binciken jin ra’ayin jama’a da aka gudanar a kasar Faransa, sakamakon binciken yace kashi hudu cikin Biyar na Faransawa sun yi imanin Francois Hollande zai sha kaye a zaben 2017 saboda matsalolin tattalin arziki da suka shafi rashin aikin yi da karin kudaden haraji.

Shugaban kasar Faransa Francois Hollande
Shugaban kasar Faransa Francois Hollande REUTERS/Christian Hartmann
Talla

Hollande mai ra’ayin Gurguzu wanda ya kada Sarkozy a zaben shugaban kasa da ya gabata yana fuskantar suka saboda tabarbarewar magance matsalar rashin aikin yi a kasar.

Binciken jin ra’ayin Jama’ar da kafafofin yada labaran Le Figaro da kafar Telebijin ta LCP suka gudanar, sakamakon yace kashi 76 cikin 100 sun bayyana Hollande a matsayin wanda ya saba alkawali, kuma kashi 68 sun ce yana da rauni wajen tafiyar da gwamnati.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.