Girka
Kungiyar ma’aikatan Girka za ta goyi bayan yajin aikin ma’aikatan kamfanoni
Kungiyar ma’aikatan kwadagon kasar Girka ta ce za ta goyi bayan yajin aikin da ma’aikatan kamfanoni masu zaman kansu za su fara a ranar 6 ga watan gobe.
Wallafawa ranar:
Talla
Kungiyar ta ce za ta yi hakan ne domin kawo karshen yadda gwamnatin kasar ke ci gaba da mika wuya ga matsalin lambar kungiyar tarayyar Turai da kuma asusun lamuni na duniya karkashin shirin tsuke bakin aljihun gwamnatin kasar.
Haka kuma ta ce bai kamata a ci gaba da zurawa hukumomin kasar ido suna ci gaba da aiwatar da wannan siyasa da suka ce tana cutar da ma’aikata da kuma al’ummar kasar ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu