Yajin aikin ma'aikata na neman gurgunta tattalin arzikin Girka
Hukumomin kasar Girka, sun rufe tashoshin radio da talabijin mallakar Gwamnati, a Ci gaba da daukar matakan tsuke bakin aljihun Gwamnati, matakin da ya jefa rudani kan halin da ma’aikata 2,700 za su shiga. Dubban mutanen gari ne suka ruga Cibiyar tashoshin dan nuna goyan bayan su ga ma’aikatan.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Kakakin Gwamnatin kasar, Simos Kedikoglu, ya bayyana kafafen yada labaran a matsayin wata rariyar da ke zubar da kudin Gwamnati.
Yanzu haka dai dimbin mutane ne suka yi cincirindo a gaban ginin ofishin Firayi ministna kasar domin nuna adawarsu da rufe tashar ta talabijin da kuma yadda suke ganin rayuwar ma'aikanta 2,700 da ke aiki a wurin na iya fadawa a cikin mummnan hali.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu