Isa ga babban shafi
Jamus

Jamus na zawarcin ma’aikata daga kasashen dake fama da matsalar tattalin arziki

Ma’aikatar kula da diban ma'aikata a kasar Jamus ta fara gayyatar likitoci da kuma masana harkar kimiyya zuwa kasarta, daga kasashen Gabashin Nahiyar Turai da ke fama da matsalar tattalin arziki. Jamus ta kasance kasa a Nahiyar ta turai da ta fi kowace kasa yawan arziki. 

Shugabar gwamnatin kasar Jamus Uwar gida Angela Markel tana jawabi
Shugabar gwamnatin kasar Jamus Uwar gida Angela Markel tana jawabi REUTERS/John Macdougall/Pool
Talla

‘‘Kasar Jamus za ta tarbi ma’aikata a fannoni daban-daban da yawansu ya kai 200,000 a duk shekara domin magance matsalar rashin ma’aikata a kasar’’ Inji shugaban dake kula da ma’aikatar diban ma’iakata, Frank- Juergen.

Yawan ma’aikata da kasar ta Jamus ta diba daga kasashen Girka da Italiya da kuma Spain ya haura da kashi takwas a shekarar da ta gabata, a cewar Juergen.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.