Isa ga babban shafi
Faransa

Jirgi dauke da gawar Philippe Verdon ya isa Paris na kasar Faransa.

A yau laraba, an dawo da gawar Philippe Verdon a birnin Paris, wato daya daga cikin Faransawa 7 da aka sace a kasar Mali, sannan aka tsinci gawarsa a cikin makwannin da suka gabata.

Ministan harkokin wajen Faransa, Laurent Fabius.
Ministan harkokin wajen Faransa, Laurent Fabius. REUTERS/John Vizcaino
Talla

Shi dai Verdon an sace shi ne a watan Nuwambar shekara ta dubu biyu da 11 a kasar Mali, kuma kwanaki kadan bayan hakan ne Kungiyar AQMI reshen kungiyar Alqa’ida a arewacin Afirka ta ce ita ce ta sace shi.

To sai dai a cikin watan Maris da ya gabata, kungiyar ta fitar da wata sanarwa da ke cewa ta kashe Verdon dan kimanin shekaru hamsin da uku a duniya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.