Magajin garin London ya ce a kada kuri'ar jin ra’ayi akan Tarayyar Turai
Magajin Garin London, Boris Johnson, ya yi kira da a gudanar da zaben jin ra’ayin akan dangantakar da ke tsakanin Birtaniya da Tarayyar Turai. Johnson ya kuma yi watsi da kiran da ake yi na cewa dunkulewan kasashen Nahiyar Turai wajen samar da mafita ga tabarbarewar tattalin arziki yankin, inda ya ce yin hakan ba demokradiya ba ne.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Magajin garin na London, ya yi wannan bayani a lokacin da ya ke jawabi a gaban masu samar da kudade sabbin hanyoyin kasuwanci ga Brussels.
“Wannan wata yarjejeniya ce wacce aka sake tattaunawa akai, ya kuma kamata a kada kuri’a domin aji ra’ayin daukacin mutanen Birtaniya.” Inji Johnson.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu