An hallaka mutane 4 cikin harbi a makarantar Yahudawa ta Faransa
Kasar Faransa na fuskanta a yanzu haka matsalolin tsaro inda bayan kasan gilla da wani da bidinga dadi ya yi a wata makarantar Yahudawa dake garin Toulouse tare da hallaka yara uku da malami daya. Hukumomin kasar sun ja damarar tabbatar da kawo karshen lamarin, inda cikin makon jiya aka hallaka jami'an tsaron.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Shuganba kasar Nicolas Sarkozy wanda ya katse yakin neman zabe tare da ziyarar inda abun ya faru, ya ce wannan bali'i ne na kasa, kuma ya yi alkawarin cafke maharin.
Jami'ai sun amince cewa akwai halaka tsakanin harbin makon jiya da kuma abun ya faru yau Litini. Wannan harbi ya jiggiga kasar ta Faransa.
A wata karamar ziyara da ya kai birnin na Toulouse Shugaba Nicolas Sarkozy, ya kaddamar da wata ayar doka inda duk fadin kasar gobe a cikin makarantu za a kebe minti guda domin tunawa da wadanda suka rasa ransu, a wannan harbi da aka yi a makarantar ta Yahudawa. Gwamnati ta sha alwashin kamo maharin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu