Isa ga babban shafi
EU-Girka

Ministocin Turai zasu gudanar da taro game da Girka

Ministocin Kudin Kasashen Turai zasu gudanar da wani taro a birnin Brussels, domin neman amincewa da matakin bayar da Tallafin kudi euro Miliyan 130 ga kasar Girka ko kuma kasar ta durkushe daga ranar 15 ga wata mai zuwa.

Fira Ministan  Luxembourg, Jean-Claude Junker  tare da Fira Ministan kasar Girka, Lucas Papademos a lokacin wani taro da suka gudanar a birnin Brussels
Fira Ministan Luxembourg, Jean-Claude Junker tare da Fira Ministan kasar Girka, Lucas Papademos a lokacin wani taro da suka gudanar a birnin Brussels © Reuters/Yves Herman
Talla

Fira Ministan Girka, Lucas Papademos yana cikin wadanda zasu halarci taron tarr Ministan kudinsa domin ganin ya samu nasarar shawo kan Ministocin, yayin da Sakataren Baitulmalin Amurka Timothy Geithner yace suna lallashin Hukumar Bada lamini ta duniya don taimakawa Girka.

Ministan kudin kasar Faransa, Francois Baroin yace akwai yiyuwar tawagar Ministocin Turai zasu amince da Tallafin da zasu ba kasar Girka.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.