Isa ga babban shafi
EU-Girka

Ministocin Turai sun sake gabatar da wasu sabbin matakai akan Girka

Ministocin kudi kasashen Turai sun sake gabatarwa kasar Girka sabbin matakai domin ceto darajar tattalin arzikinta, amma kungiyoyin kwadago a kasar Girka sun shirya gudanar da yajin aikin gama-gama domin nuna adawa da matakin tsuke bakin aljihun gwamnati. 

Taron ministocin kasashen Turai a Brussels, Evangelos Venizelos tare da shugaban taron  Jean-Claude Juncker,
Taron ministocin kasashen Turai a Brussels, Evangelos Venizelos tare da shugaban taron Jean-Claude Juncker, Reuters/Yves Herman
Talla

Jagoran tattaunawar Ministocin kudin kasashen turai yace sabbin matakan zasu hada da kudi euro biliyan 130 da za’a ba Girka domin ceto darajar tattalin arzikinta.

Jean-Claude Juncker yace ya zama dole 'Yan majalisun Girka su amince da matakan tsuke bakin aljihu a zamansu na ranar Lahadi.

Sai dai kungiyoyin kwadago a kasar Sun kira wani yajin aikin sa’o’I 48 da za’a fara a yau Juma’a domin nuna adawa da matakan tsuke bakin aljihun.

Mista Juncker, Fira ministan kasar Luxembourg yace akwai bukatar ‘yan siyasa a kasar Girka su bada tabbacin cim ma sabbin sauye sauye bayan kammala zaben da za’a yi a kasar a watan Afrilu.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.