MU zagaya Duniya: Kotun daukaka kara a Najeriya ta soke zaben gwamnan jihar Kano
Wallafawa ranar:
Kunna - 19:55
Ciki Shirin wannan makon za a ji cewar Kotun Daukaka karar Najeriya ta tabbatar da hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben Kano da ya karbe kujerar Gwamnan jihar daga hannunn Abba Kabir Yusuf na NNPP ya mika ta zuwa Nasir Yusuf Gawuna na APC.Kasar Ghana ta bukaci hadin gwiwar kasashen Afirka domin tilasta wa kasashen da suka yi wa nahiyar mulkin mallaka biyansu diyya akan yadda suka azabtar da su da cinikin bayi.
A Gabas ta tsakiya kuwa Fira Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ne ya zargi mayakan Hamas da dakile duk wani yunkuri na takaita yawan rayukan fararen hular da suke salwanta a Zirin Gaza.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu