Masarautunmu
Sarakuna a kasar Hausa da sauran yankunan kasashen Duniya suna da mutukar Muhimmaci ga al'ummarsu Akan haka ne kuma muka ga ya dace mu fito da wannan shirin domin farfado da darajarsu da muhimmacinsu ga ci gaban al'ummar domin babu wanda talaka yafi kusa da shi irin Sarkin garinsa kuma idan aka fahimci haka Sarakuna zasu taka rawa sosai domin sauya al'amurra a cikin kasa.
Ci gaban karatuSaurari kashin karshe
Daukacin kashi-kashi
-
A Najeriya yan bindiga sun sako sarkin Gindiri a Jihar Plateau
A Najeriya, bayan share tsawon kwanaki 5 a hannun masu garkuwa da shi, a sanyin safiyar yau juma’a basaraken gargajiya na masarautar Gindiri a jihar Plateau Mai Martaba Charles Mato Dakat, ya kubuta inda ya koma a cikin iyalansa.Da farko dai an ruwaito cewa wadanda suka yi garkuwa da basaraken sun bukaci a biya milyan 50 a matsayin kudin fansa kafin su sake shi, to amma makusantan sarkin sun ce ba a biya ko sisin kobo ba. Daga Jos, ga rahoton da Tasiu Zakari ya aiko mana.31/12/202101:31 -
Sarakuna da wakilan farar hula na zaman neman zaman lafiya a Nijer
A Jamhuriyar Nijar, wakilai da suka hada da sarakunan gargajiya, kungiyoyin fararen hula da kuma sauran magabata ne suka halarci wani taro, wanda ya yi nazari dangane da yadda za a yi tattalin zaman lafiya, lura da yadda wasu yankunan kasar ke fama da rikici.Wakilinmu a Damagaram/Zinder Ibrahim Malam Tchillo, ya hada mana wannan rahoto.31/12/202101:35 -
Kade-kade da al'adu
Shirin kade-kade da al'adu na zuwa maku ne daga ssahen hausa na rfi a kowanne Mako tare da Hauwa Kabir, a yi sauraro lafiya21/03/201519:53 -
Dalilan da suka sa Sarakuna basa sauka daga mulki a kasar Hausa kashi na 2
Shirin Daga Masatun mu shiri ne da ke leka masarutun da suka shahara aduniya.Shirin na wannan makon, zai ci gaba da duba yadda wasu sarakuna a kasashen duniya, kan sauka daga gadon sarautar, don bar wa magadan su, su ci gaba da mulki kasar tasu.A shirin na makon da ya gabata, mun duba yadda a kasar Belgium, Sarki Albert II ya sauka daga mukamin shi don radin kan shi, inda ya mika wa dan shi yarima Philippe, a cikin wannan shekarar.Ita ma Sarauniya Beatrix ta Hollanda, ta sauka daga mukamin ta inda ta mika wa dan ta Willem-Alexander madafun ikon masarautar.A kasar Qatar ma sarki Hamad bin Khalifa Al Thani, ya ajiye muklamin shi ya mika wa dan shi, Sheikh Tamim a cikin shekarar ta 2013.To wannan shirin ya fara duba dalilan da suka sa sarakunan kasar Hausa, basa yarda su bar gadon sarautar tun suna da rai.Prof Aliyu Muhammad Bunza, Malami a sashen koyar da Harsunan Najiriya, a jami’ar Usman Dan Fodiyo da ke Sokoto, ya yi bayani kan wannan, don haka sai a biyo mu cikin shirin, wanda shine kashi na 2 kuma na karshe, Tare da Nasiruddeen Muhammad, don jin karin bayani.A yi saurare lafiya.23/08/201310:00 -
Dalilan da suka sa Sarakuna basa sauka daga mulki a kasar Hausa kashi na 1
Shirin Daga Masatun mu shiri ne da ke leka masarutun da suka shahara aduniya.Shirin na wannan makon, zai duba yadda wasu sarakuna a kasashen duniya, kan sauka daga gadon sarautar, don bar wa magadan su, su ci gaba da mulki kasar tasu.A kasar Belgium, Sarki Albert II ya sauka daga mukamin shi don radin kan shi, inda ya mika wa dan shi yarima Philippe, a cikin wannan shekarar.A dai cikin shekarar, Sarauniya Beatrix ta Hollanda, ta sauka daga mukamin ta inda ta mika wa dan ta Willem-Alexander madafun ikon masarautar.A kasar Qatar ma sarki Hamad bin Khalifa Al Thani, ya ajiye muklamin shi ya mika wa dan shi, Sheikh Tamim a cikin shekarar ta 2013.To wannan shirin zai duba dalilan da suka sa sarakunan kasar Hausa, basa yarda su bar gadon sarautar tun suna da rai.Prof Aliyu Muhammad Bunza, Malami a sashen koyar da Harsunan Najiriya, a jami’ar Usman Dan Fodiyo da ke Sokoto, ya yi bayani kan wannan, don haka sai a biyo mu cikin shirin, da shine kashi na farko, Tare da Nasiruddeen Muhammad, don jin karin bayani.A yi saurare lafiya.16/08/201310:05 -
Bukin cika shekaru 50 na sarkin Kano a kan karagar mulki
Shirin na yau zai leka masarautar Kanon dabo, da ke Arewacin Nigeria, inda a karshen makon da ya gabata, aka yi bukin cika shekar 50, da mai martaba Alhaji Dr Ado bayero ya dare gadon sarautar ta Kano.Cikin wannan shirin, Nasiruddeen Muhammad ya leka masauratar ta Kano, ida aka yi shagulgulan, kuma ya sami tattaunawa da masu ruwa da tsaki a bukin, a yi saurare lafiya.21/06/201310:00 -
Cikar Mai martaba sarkin Kano Dakta Alhaji Ado Bayero Shekaru 50 kan karagar masarautar Kano
Shirin Daga Masarautunmu, tare da Garba Aliyu Zaria, a wannan karo ya mayar da hankali ne kan bukukuwan cikar Mai Martaba Sarki Kano Alhaji Dakta Ado Bayero shekaru 50 a kan karagar masarautar Kano a Tarayyar Najeriya.15/06/2013 -
Masarautar Kwanni a Jamhuriyar Nijar.
Shirin Daga Masarautunmu na wannan karo, Garba Aliyu Zaria ya ci gaba ne da yi wa masu sauraro bayani a game da masarautar Kwanni da ke cikin jihar Tawa a Jamhuriyar Nijar.31/05/201310:09 -
Tarihin Masarautar Machina dake Jihar Yobe a Najeriya
Masarautar Machina dake Jihar Yobe a Najeriya. Wacce ke karkashin jagorancin Alhaji Bashir Al bashir Machina.26/04/201310:13 -
Shirin Daga Masaratunmu
Tarihin Masarautar Machina, gari mai Macizai da Dutse mai amarya. Tarihi daga bakin Mai Martaba Sarkin Machina Alhaji Bashir al-Bashir Bukar OON. Ya tattauna da sashen Hausa na RFI a fadarsa, lokacin bukin Al'adun gargajiyar su na bana.05/04/201310:03 -
Tarihin Masarautar Potiskum dake Jihar Yobe a Tarayyar Najeriya
Tarihin Masarautar Potiskum dake Jihar Yobe a Tarayyar Najeriya22/02/201310:26 -
Tattaunawa da Mai Martaba Sarkin Argungu, Alhaji Sama'ila Muhammadu Mera.
Shirin Daga Masarautunmu a wannan satin ya leka masarautar Argungu, da ke Jihar Kebbi a tarayyata Najeriya, inda aka tattauna da Mai Martaba, Alhaji Sama'ila Muhammadu Mera.28/09/201210:00 -
Masarautar Daura shiri na 2
Wannan shiri ne na biyu game da Masarautar Daura a Jahar Katsina Tarayyar Najeriya. Masarautar mai dimbin tarihi a kasar Hausa. Shirin ya zanta da Sarkin Daura Mai Martaba Faruk Umar Faruk tare da kai ziyara rijiyar Kusugu.06/04/201210:06 -
Masarautar Daura shiri na 1
Shirin Masarautunmu ya kai ziyara ne fadar Sarkin Daura Faruk Umar Faruk wanda ya tattauna da Sarkin domin samun tarihin rayuwar shi da masarautar Daura. Shirin kuma ya kai ziyara a rijiyar Kusugu mai dimbin tarihi a Daura.30/03/201210:29 -
Masarautar Damagaram
Shirin Masarautunmu ya tattauna ne da sarkin birnin Damagaram a Jamhuriyyar Nijar Alh. Abubakar Ummaru Sanda wanda ya bada tarihin masarautar da kuma yadda ya gaji mahaifin shi.10/02/201209:53
Masarautunmu
Sarakuna a kasar Hausa da sauran yankunan kasashen Duniya suna da mutukar Muhimmaci ga al'ummarsu Akan haka ne kuma muka ga ya dace mu fito da wannan shirin domin farfado da darajarsu da muhimmacinsu ga ci gaban al'ummar domin babu wanda talaka yafi kusa da shi irin Sarkin garinsa kuma idan aka fahimci haka Sarakuna zasu taka rawa sosai domin sauya al'amurra a cikin kasa.