Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Amb Ibrahim Kazaure kan janye takunkumin ECOWAS ga kasashen Nijar, Mali da Burkina Faso

Wallafawa ranar:

Kungiyar ECOWAS ta sanar da janye takunkumin karya tattalin arzikin da ta sanyawa kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso, yayin da ta bukaci sojojin da suka yi juyin mulki a wadannan kasashe da su dawo teburin tattaunawa domin samo hanyar mayar da mulkin dimukiradiya a cikin su. Shugabannin ECOWAS sun ce an cire takunkumin ne saboda dalilan jinkai, kuma matakin ya kawo karshen hana zirga zirgar jiragen sama da bude asusun ajiyar wadannan kasashe guda 3.

ECOWAS ta janye takunkumin da ta sanya wa kasashen da sojoji suka yi wa juyin mulki.
ECOWAS ta janye takunkumin da ta sanya wa kasashen da sojoji suka yi wa juyin mulki. AFP - KOLA SULAIMON
Talla

Dangane da tasirin wannan mataki, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ambasada Ibrahim Kazaure, masanin harkar diflomasiya.

Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawar su ta gudana.....

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.