Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Benin ta dakatar da kwashe kaya daga tashar jiragen ruwan Cotonou zuwa Nijar

Wallafawa ranar:

Gwamnatin Jamhuriyar Benin ta ce ba za ta bari a kwashe kayayyakin da aka sauke a tashar jiragen ruwan Cotonou zuwa Nijar ba, amma a maimakon haka za ta bai wa ‘yan kasuwar Nijar damar karkata akalar kayayyakin zuwa wasu kasashe, ta hanyoyin mota ko jiragen ruwa.

Tashar jiragen ruwan Cotonou da ke jamhuriyar Benin, 28/05/2019
Tashar jiragen ruwan Cotonou da ke jamhuriyar Benin, 28/05/2019 © Prosper Dagnitche / AFP
Talla

 

A sanarwar da ta fitar karshen mako, hukumar kula da tashar jijagen ruwan Cotonou ta kuma bai wa ‘yan kasuwar Nijar damar sayar da kayayyakinsu a Benin idan har ba za su karkata akalarsu zuwa wata kasa ba. 

Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Yacouba Dan Maradi, shugaban kungiyar ‘yan kasuwa da ke shigar da kaya a Nijar, domin jin yadda suke kallon wannan mataki. Ga kuma zantawarsu. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.