Alh. Barkire: Kan makalewar motocin dakon kaya na Nijar
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:23
Yanzu haka dimbin motocin sufuri da dama ne dauke da kaya suka tsaya cak a kan titunan Jamhuriyar Nijar, yayin da wasu suka makale a tashar jiragen ruwan Cotonou, sakamakon wani sabani da ya kunno kai tsakanin masu motocin sufuri na kasar da kuma wadanda aka bai wa kwangilar sufurin bututun man fetur da China ke shirin shimfidawa daga Nijar zuwa Jamhuriyar Benin.
A kan wannan batu ne, AbdoulKarim Ibrahim Shikal ya tattauna da Alhaji Hima Barkire, daya daga cikin shugannin kungiyar masu motocin dakon kaya a jamhuriyar Nijar.
Ku latsa alamar sautin domin sauraren cikakkiyar hirar
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu