Bakonmu a Yau
Dan Majalisar Nijar Murtala Alhaji Mamuda kan kammala aikin Majalisar
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:34
A Jiya Laraba ne majalisar dokokin kasar Jamhuriyar Nijer ta kawo karshe wa’adin aikinta na tsawon shekaru 5. Majalisar da aka zaba a 2016 zuwa 2021, ta rufe kofofinta ne tare da jawabin da shugabanta Husaini Tinni ya yi a zauren majalisar dake birnin Yamai. To domin jin Irin muhimman ayuka na gari da za a shaidi majalisar da aikatawa, Mahaman Salisu Hamisu ya tattauna da dan majalisar dokoki Murtala Alhaji Mamuda.