Isa ga babban shafi
Nijar

Mayakan Boko Haram sun kai sabon farmaki kan yankin Diffa

Rahotanni Daga Jamhuriyar Nijar sun ce mayakan Boko Haram sun kashe mutane 7, tare da sace mata biyu a Yankin Diffa.

Wasu dakarun sojin Nijar yayin tunkarar garin Bosso da ke kudu maso gabashin kasar, a gaf da iyakar Najeriya.
Wasu dakarun sojin Nijar yayin tunkarar garin Bosso da ke kudu maso gabashin kasar, a gaf da iyakar Najeriya. AFP Photo/ISSOUF SANOGO
Talla

Kungiyar Alternative tace mayakan sun kai harin ne daren ranar Jiya Asabar, inda suka kona kasuwa da gidaje da dama.

Rahotanni sun ce ko a ranar Alhamis, sai da mayakan na Boko Haram suka kai hari kauyen Karidi dake kusa da iyakar Najeriya, inda suka kashe mutane 8, cikin su harda mace guda.

A ranar 9 ga watan Maris, mayakan sun hallaka wasu dakarun sojin Nijar 9 a wani farmaki da suka kai musu a yankin na Diffa, kawanaki kalilan bayan da sojin na Nijar suka hallaka mayakan na Boko Haram guda 33.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.