'Yan ta'adda sun kashe mutane, bayan sace 24, da kona kasuwa da gidaje a Katsina
Wasu ‘yan ta’adda sun kashe mazauna kauyen Gangara da ke karamar hukumar Jibia 5 tare da raunata wasu 7 a wani hari da suka kai a daren ranar Alhamis a jihar Katsina. Maharan sun kuma yi awon gaba da mazauna yankin 24, yawancinsu mata da kananan yara.
Wallafawa ranar:
A wannan hari,’yan ta’addan sun kuma kona gidaje shida da kuma kasuwar yankin.
Hakimin unguwar Gangara, Aliyu Abubakar, ya shaida jaridar PREMIUM TIMES a Najeriya ta wayar tarho cewa, dukkan mutanen biyar da aka kashe, mazan aure ne.
“Yan ta’addan sun kai harin ne da misalin karfe 10 na dare tare da harbin daga Sabon Garin Gangara, inda suka kashe mutum daya.
Mutanen garin sun bayyana harin na baya-baya nan a matsayin mummuna. Mutane bakwai sun samu munanan raunuka,wandada aka kai wasu asibitocin kashi da kwararru yayin da wasu kuma suka kasance a asibitin Koyarwa na Tarayya suna karbar kulawar likitoci.
Maharan sun zabi wadanda za su yi garkuwa da su ba tare da sun bayyana dalilin ba.
Basaraken garin ya ce an binne gawarwakin wadanda suka mutu tare da taimakon ‘yan banga.
Ya ce zuwan ’yan banga ne ya kawo karshen kashe-kashen da ake yi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu