Isa ga babban shafi

Gobe Kotun Koli za ta bayyana ainihin wanda ya lashe zaben 2023

Kotun Koli ta sanya gobe Alhamis a matsayin ranar da za ta yanke hukunci kan shari’ar da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, da Peter Obi suke kalubalantar nasarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben 2023.

Atiku Abubakar da kuma Peter Obi su ke kan gaba wajen kalubalantar sakamakon zaben, inda su ke neman a soke zaben, saboda zargin an tafka magudi.
Atiku Abubakar da kuma Peter Obi su ke kan gaba wajen kalubalantar sakamakon zaben, inda su ke neman a soke zaben, saboda zargin an tafka magudi. © Daily Trust
Talla

 

Atiku wanda shi ne dan takarar shugaban kasa na babbar jam’iyyar adawa ta PDP ya shigar da karar ne kamar takwarana na Jam’iyyar LP, Mista Peter Obi.

Atiku da Peter Obi kowannensu na ikirarin shi ne ya lashe zaben na ranar 25 ga watan Fabrairu, 2023 da kuri’u mafiya rinjaye, duk da cewa Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta sanar cewa Tinubu ne ya yi nasara, aka rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayu.

Daraktan Yada Labarai na Kotun Koli, Festus Akande ya sanar a ranar Laraba cewa a ranar Alhamis alkalan kotun za hu yanke hukunci kan shari’ar zaben na ranar 25 ga watan Fabrairu.

A ranar Litinin PDP da LP da ’yan takararsu suka gabatar da shaida a gaban kotun koli, wadda ta yi watsi da karar Jam’iyyar APM da dan takararta, Chichi Ojei, bayan sun janye kararsu.

Atiku, Obi da jam’iyyunsu, sun daukaka kara zuwa kotun koli ne saboda rashin gamsuwarsu da hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa na ranar 6 ga watan Satumba, wanda ya yi watsi da kararsu saboda rashin gamsassun hujjoji.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.