Isa ga babban shafi

Rundunar ‘Operation Hadarin Daji’ ta ceto daliban jami’ar tarayya na Gusau

A Najeriya ,sojojin da ke aiki da rundunar ‘Operation Hadarin Daji’ sun ceto daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ke jihar Zamfara, bayan sun yi artabu da ‘yan ta’adda da safiyar yau Lahadi. 

'Yan sandan Najeriya a jihar Zamfara.
'Yan sandan Najeriya a jihar Zamfara. © REUTERS/Afolabi Sotunde/File Photo
Talla

Rahotanni na nuni cewa an yi garkuwa da daliban ne a ranar Asabar a lokacin da ‘yan ta’addan suka kai farmaki a wasu gidajen kwanan dalibai da ke Sabon Garin Damba, Gusau, inda suka tafi da dalibai hudu.

Wasu daga cikin daliban makarantar Jangebe da 'yan bindiga suka taba sacewa a Zamfara.
Wasu daga cikin daliban makarantar Jangebe da 'yan bindiga suka taba sacewa a Zamfara. AP - Sunday Alamba

Wannan dai shi ne karo na biyu da 'yan ta'addan za su kai hari a dakunan kwanan dalibai na jami'ar cikin kasa da kwanaki 30. Kakakin rundunar sojojin Najeriya ta Birged 1 da ke Gusau, Ibrahim Yahaya, ya ce yayin da biyu daga cikin daliban suka tsere a yayin musayar wuta tsakanin sojojin da 'yan ta'addar, sojojin sun ceto sauran daliban biyun da ke hannun yan ta’adda yayin arangamar.  

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.