Isa ga babban shafi

‘Yan bindiga sun kutsa kai jami’ar Gusau inda suka yi garkuwa da dalibai da malamai

Bayanai daga jihar Zamfara a Najeriya na cewa ‘yan bindiga sun kutsa kai jami’ar gwamnatin tarayya da ke Gusau inda suka yi garkuwa da dalibai da malamai da dama. ‘Yan bindigar masu matukar yawa sun kewaye unguwar sabon gida dake karamar hukumar Bungudu, kafin daga bisani su kutsa kai cikin jami’ar. 

'Yan sandan Najeriya a jihar Zamfara.
'Yan sandan Najeriya a jihar Zamfara. © REUTERS/Afolabi Sotunde/File Photo
Talla

Rahotanni sun ce ‘yan bindigar sun hari dakunan kwanan dalibai guda uku, kuma sun kwashe dukannin daliban da ke cikin su. 

Duk da cewa jami’an sojoji sun mayar da martani kan harin amma duk da haka ‘yan bindigar sun yi nasarar tafiya da daliban har ma da wasu daga cikin malaman su. 

An gano cewa ‘yan bindigar sun raba kan su biyu, inda wasu suka tafi da dalibai, wasu kuma suka tsaya suka tunkari sojoji. 

Jami’ar gwamnatin tarayya da ke Gusau
Jami’ar gwamnatin tarayya da ke Gusau Fugus facebook

Wasu ganau sun shaidawa manema labarai cewa ‘yan bindigar sun mamaye unguwar da misalin karfe 3 na dare, kuma suka bude wuta harbin kan mai uwa da wabi, bayan kowa ya gudu ne kuma suka kutsa kai cikin jami’ar. 

Rundunar ‘yan sandan jihar ta ce har yanzu babu tabbas game da adadin dalibai da malaman da ‘yan bidnigar suka tafi da su, amma dai ana kan bincike. 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.