Isa ga babban shafi

Jami'an tsaron Najeriya sun kama 'yan daba da dama yayin zaben gwamnoni

Jami’an ‘yan sandan Najeriya sun cafke mutane da dama da suka yi yunkurin haddasa rikici a yayin gudanar da zaben gwamnonin jihohi a sassan kasar, ciki har da Kano da Lagos. 

Jami'an tsaron Najeriya yayin aikin sintiri a lokacin zabe.
Jami'an tsaron Najeriya yayin aikin sintiri a lokacin zabe. AP - Sunday Alamba
Talla

A jihar Kano kadai, jami’an ‘yan sanda sun kama jumillar mutane 161 da suka hada da wani dan majalisar jihar, Isyaku Ali-Danja bisa zargin su da kokarin haddasa hatsaniya a yayin da jama’a suka fito domin kada kuri’unsu a ranar Asabar. 

Bayanai na cewa, dan majalisar mai wakiltar mazabar Gezawa, shi ne ya jagoranci ayarin ‘yan daba domin kai hari kan ofishin Hukumar Zabe ta INEC a Karamar Hukumar Gezawa. 

Hakan nan a jihar Lagos da ke kudancin Najeriya, jami’an ‘yan sandan sun damke mutane 17 cikinsu har da wata mace guda bayan sun yi yunkurin tayar da hankali a yayin zaben. 

‘Yan sandan na Lagos  sun kuma yi nasarar kwato akwatinan zabe da wasu ‘yan jagaliya suka yi awon gaba da su. 

A bangare guda, Jami’an Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Najeriya EFCC sun kama akalla mutane 65 a sassan  jihohin kasar 28 a yayin gudanar da zaben na gwamnoni saboda yadda suka yi ta rudar mutane da kudi suna saye kuri’unsu. 

Jami’an na EFCC sun kwace wasu daga cikin kayayyakin sayen kuri’un kamar a jihar Sokoto, inda suka kwace turamen atamfa da aka yi ta raba wa mata a matsayin cin hanci. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.