CBN zai soke baiwa bankunan Najeriya kudaden kasashen waje
Babban Bakin Najeriya CBN ya ce wani lokaci cikin wannan shekara zai soke saidawa bankunan kasar kudaden kasashen waje kamar yadda aka saba.
Wallafawa ranar:
Kunna - 01:06
Gwamnan babban bankin Godwin Emefiele wanda ya sanar da haka a Abuja yace, zasu taimawa bankunan hanyoyin samun kudaden da kansu.
Hakan na zuwa ne bayan da asusun bada lamuni na duniya IMF ya sake yin kira ga gwamnatin Najeriya da ta janye tallafin Man fetur da kuma cire farashin canji kudaden ketare a hukumance.
Matakin da masana tattalin arziki irinsu Dakta Isa Abdullahi na jami’ar Tarayya ta Kashere dake Gombe ke ganin da lale. Kuna iya latsa alamar sauti domin sauraron abin da masanin ke cewa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu