Isa ga babban shafi
Kamaru

Dakarun Najeriya sun kame manyan kwamandojin Boko Haram

Rundunar sojin Najeriya tace dakarunta sun kame wasu mayakan Boko Haram 16 a yankin Pulka dake karamar hukumar Gwoza.

Wasu dakarun sojin Najeriya akan hanyar Konduga zuwa Bama a jihar Borno. 31/8/2016.
Wasu dakarun sojin Najeriya akan hanyar Konduga zuwa Bama a jihar Borno. 31/8/2016. REUTERS/Afolabi Sotunde/File Photo
Talla

Dakarun Najeriyar sun kai samamen ne a ranar 20 gawatan Oktoban 2019, inda suka kame mayakan, ciki har da wasu manyan kwamandojin kungiyar ta Boko Haram da ke cikin jerin wadanda ake nema ruwa a jallo.

Mai magana da yawun sojojin Najeriya Kanal Aminu Iliyasu, ya ce kwamandojin masu tada kayar bayan da suka shiga hannu sun hada da Lawan Abubakar Garliga, mutum na 41 da kuma Bayaga Manye na 90, dukkaninsu da ke cikin manyan jagororin kungiyar Boko Haram da ake nema ruwa a jallo.

Kakakin sojin Najeriyar Kanal Iliyasu, ya ce binciken farko da suka gudanar, ya nuna cewa, wasu daga cikin mayakan da suka kama, na cikin wadanda suka kai kazaman hare-hare a Pulka da Gwoza, sai kuma yiwa wasu jami’an ‘yan sanda kisan gilla a shekarun baya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.