'Yan bindiga sun hallaka mutane 9 a Birnin Gwari
Wasu ‘yan bindiga da ake zargin barayi ne sun hallaka mutane 9, da raunata wasu da dama a lokacin da suka afka wa kauyen Kaguru da ke yankin Birnin Gwari a jihar Kaduna, da ke arewacin Najeriya.
Wallafawa ranar:
Wasu mutanen da dama ne suka arce cikin dazuka, yayin da wadansu ke gudun hijira a kauyukan da ke makwaftaka.
Isyaku B. Aliyu tsohon shugaban karamar hukumar, ya shaidawa Sashin Hausa na RFI cewa, maharan sun cinnawa gidaje da dama a kauyen wuta, har yanzu kuma ba’a gano wasu daga cikin mutanen da suka bace ba, bayan da suke tsere cikin daji.
Aliyu ya kara da cewa kwanaki goma da suka gabata, wasu ‘yan bindiga sun kai hari cikin dare kan kauyen Kirazu, a karamar hukumar ta Birnin Gwari, inda suka hallaka yaro daya da kuma jikkata wasu mutane da dama.
'Yan bindiga sun hallaka mutane 9 a Birnin Gwari
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu