Najeriya: Shirin samawa iyalai masu karamin karfi gidaje
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:29
Mukaddashin Shugaban kasar Najeriya, Farfesa Yemi Osinbajo ya ce gwamnati ta kaddamar da shirin samawa iyalai gidaje a kan Naira biliyan 100 karkashin tsarinta na raya kasa. Mista Osinbajo ya sanar da wannan shiri ne, a lokacin bikin cikar gwamnatinsu shekaru 2 akan karagar mulki, idan ya zayyana nasarorin da suka cimma da shirin da ke tafe don raya kasa. Kamar yadda Mukadashin ya sanar, duk wanda ke karban albashin naira dubu 30 na da damar shiga tsarin. To sai dai a tattaunawarsu da Umaymah Sani Abdulmumin, Sakataren tsare-tsare a kungiyar kwadago ta NLC Comorade Nasiru Kabir, ya ce da wuya shirin ya yi tasiri.